INNA LILLAHI.ANGANO GAWAR HANIFA WACCE AKASACE KWANAKIN BAYA A KANO


 An gano gawar yarinyar da aka sace a birnin Kano da ke arewacin Najeriya ranar 4 ga watan Disamban 2021.

Mahaifin yarinyar ya tabbatar wa da BBC cewa an gano hakan ne ta hanyar gano wanda ya sace ta É—in, bayan da ya zayyana wa jami'an tsaro yadda komai ya wakana.

Mahaifin Hanifa ya ce a yanzu haka an tono gawar Æ´ar tasa wacce mutumin da ya sace ta ya kashe ya kuma binne ta tun kwana biyar da sace ta.

Wanda ake zargi da kisan na gaban Æ´an sanda yana fuskantar tuhuma, kuma tuni ya fara bayani kan yadda aka yi ya kashe ta.


Mahaifin Hanifa ya ce tuni aka tono gawar Hanifa da mutumin ya binne, don gudanar da bincike a kanta. Sannan kuma an sake binne ta kamar yadda shari'a ta tanada a maƙabartar Ƴan Kaba.

Ya kuma shi mai lafin ya shaida wa jami'an tsaro cewa ya sanya mata shinkafar ɓera ne tare da ƙunshe ta a leda ya kuma binne ta a rami.

©Fatimiyyaa 


Comments