SHARIF RABIU USMAN BABA YACIKA KWANAKI DUBU DAYA DA RASUWA


 Allah Sarki Rayuwa:Cikar Sharif Rabi'u usman Baba kwana dubu da Rasuwa" Tarihin Rayuwar sa dakuma wakokin shi

February 07, 2022

Allah Sarki Rayuwa:Cikar Sharif Rabi'u usman Baba kwana dubu da Rasuwa" Tarihin Rayuwar sa dakuma wakokin shi



 Kwanan watan yazo da kamanceceniyar lambobi kuma yayi daidai da cika kwanaki 1,000 cif da rasuwar Sharif Rabi'u Usman Baba "Mutuwa bata bar talakawa ba ta yanke talaucin su, Ta kan bi sarakai ma mutuwa ta raba su da mulkin su, Um uhum wayyo kai na, Mutuwa Riga ce ba ta fita.”


 

Baitin waÆ™ar mutuwa kenan ta shahararren mawaÆ™in yabon Manzon Allah  (SallalLahu AlaiHi Wa AaliHi Wa Sallam), Sharif Rabi'u Usman Baba, wanda Allah Ya yi wa rasuwa a ranar Alhamis 9 ga Mayu, 2019 bayan wata gajeriyar rashin lafiya. Ya rasu a gidan sa da ke unguwar Janbulo a cikin garin Kano.

 

Marigayin, mai shekaru 52  a duniya a wani Æ™aulin kuma 54, ya rasu ya bar mata uku a wani Æ™aulin kuma Mata 4, da ƳaÆ´a 13 ko kuma 18.

 

Kafin rasuwar sa dai shi ne shugaban Æ™ungiyar sha’irai da ake kira Jama'atu Shu’ara’il Islam Muddahi Sayyidul Anam (SallalLahu AlaiHi Wa AaliHi Wa Sallam).

 

Rasuwar sa ta jijjiga duniyar Musulmi baki É—aya, domin kuwa Sharif Rabi’u Usman Baba ya zama fitaccen MawaÆ™in Janabin ANNABI (SallalLahu AlaiHi Wa AaliHi Wa Sallam) sakamakon irin salon da ya zo da shi da kuma tafiya da zamani. Irin salo da jigon da ya ke amfani da shi wajen faÉ—akarwa, ilimantarwa ta hanyar waÆ™oÆ™in sa, ya sa ya zamo abin karÉ“uwa a wajen jama’a. Don haka babu wani kokwanto shi wani jigo ne a cikin waÉ—anda su ka kawo wa É“angaren waÆ™oÆ™in Musulunci juyin-juya-hali.

 


Tauraruwar Sharif Rabi’u Usman Baba ta fara haskawa ne tun cikin shekarar 1985, a shekarar 1998 ya yi shaharar da babu wani Sha’iri da za a haÉ—a shi da shi a fagen waÆ™a.

 

Ya yi waÆ™oÆ™i masu adadi da yawa, kamar irin su:- Tauhidi Babu tantama, Mutuwa, Tsumagiya, Sha yabo, Majalisi, Wakar Sadiya, Zumunci, Tambaya, Sharifai, Fadima, Garkuwa, Batijaniya, Bakadiriya, Fiyayya, Sayyadil Wara, Zuma, da sauran su, amma dai waÆ™ar da ta Æ™ara haska tauraruwar sa itace "Dukkan Mai Matsayi Wajen Ilahu Ba Zai Kai Ka Ba, Dan Amina" 


 

 

Fitowar wannan waÆ™a ta sauya alÆ™iblar matasa da yara Æ™anana, domin kuwa a lokacin waÆ™oÆ™in da su ke tashe kuma su ka fi karÉ“uwa ga matasa da yara su ne waÆ™oÆ™in Indiya da na Sudan, waÉ—anda ana sauraren su ne ba don ana fahimtar abin da su ke faÉ—a ba sai dai son nishaÉ—i kawai. Amma fitowar wannan waÆ™ar ta Sharif Rabi'u Usman Baba da sauran waÆ™oÆ™in sa da su ka biyo bayan ta ya kawar da waÆ™oÆ™in Indiya da na Sudan daga bakin matasa da Æ™ananan yara, don haka duk lokacin da za ka ji yara su na waÆ™a don nishaÉ—i sai ta yabon Manzon Allah (SallalLahu AlaiHi Wa AaliHi Wa Sallam). Kuma hakan ya sa matasa da dama su ka rungumi É—abi’ar tsara waÆ™oÆ™in yabon Janabin Manzon Allah (SallalLahu AlaiHi Wa AaliHi Wa Sallam).

 

Kafin wani lokaci sai ga shi a birnin Kano da sauran jihohi an samu masu yabon Manzon Allah (SallalLahu AlaiHi Wa AaliHi Wa Sallam) ba su da adadi. 

 

Tafiya da zamani ta sa Sharif Rabi’u Usman Baba ya daÉ—e ya na jan zaren sa, domin kuwa a farkon waÆ™ar sa ya fara ne babu KiÉ—an Bandiri, amma ganin Ƙadirawa da su ke yin waÆ™a da bandiri su na karÉ“uwa sai shi ma ya juya ya shigar da Bandiri cikin waÆ™ar sa, duk kuwa da cewa a lokacin ya sha suka a wajen Tijjanawa da su ke ganin Ƙadirawa ne su ke kaÉ—a Bandiri, a tafiyar Tijjaniyya babu KiÉ—an Bandiri. Amma dai ya tafi a hakan tare da ba su amsar da ya ke ganin ita ce hujja a gare shi.


A lokacin da kiÉ—an fiyano ya fara tashe, nan ma Sharif Rabi’u Usman Baba bai yi Æ™asa a gwiwa ba, sai ya É—auki salo don ganin kada waÆ™oÆ™in finafinan Hausa da su ke tashe a lokacin su rufe irin nasa. Don haka shi ma sai ya fara waÆ™a da kiÉ—an fiyano inda a nan ma ya yi ta samun suka, sai dai ya kare kan sa da waÆ™oÆ™in Larabawa na yabon Manzo da su ke yi da kiÉ—a. Ya nuna cewar waÆ™ar sa da fiyano a duniyar Musulunci abu ne karÉ“aÉ“É“e, in dai za a bi tsarin da ya dace. (A lokacin har yayi Ƙasida É—auke da muryar Sheikh ÆŠahiru Usman Bauchi) inda yake bada fatawa akan halascin hakan.

 

Marigayin Mutum ne da ya san Ƴancin sa, don haka bai yarda zama cikin rashin Ƴanci ba, domin kuwa an yi wani lokaci da duk shaharar da MawaÆ™i ya yi to Ƴan kasuwar da su ke buga Kaset a Kasuwar Ƙofar Wambai su ke kallon su ne kawai su ka É—aga shi. Amma shi da su ka kawo masa wasu dokoki ya ga ba zai amince da su ba sai su ka raba hanya. Sai ya buÉ—e Tsumagiya Studio a Unguwar Gwammaja, wanda duk mutumin da ke son waÆ™oÆ™in sa ya je can ya saya saboda Ƴan kasuwa sun daina buga waÆ™oÆ™in sa, hakan bai sa Sha'irin ya koma baya ba, sai ma shaharar sa ta yi gaba. 

 

HaÆ™iÆ™a Sharif Rabi’u mutum ne da ya yi rayuwar sa cikin shahara kuma har ya koma ga Allah tauraron sa bai dusashe ba. Domin kuwa da aka bayyana rasuwar sa a soshiyal midiya, sai masu hulÉ—a da shafuka su ka yi ta saka hotunan sa da kuma rubuce-rubuce na alhini da miÆ™a ta’aziyya ga al’ummar Musulmi a game da rashin sa. 


 

 

Lallai duniyar Musulmi ta yi rashin babban MawaÆ™in Janabin Sayyiduna RasululLahi (SallalLahu AlaiHi Wa AaliHi Wa Sallam). Kuma za a daÉ—e tarihi bai manta da Sharif Rabi’u Usman Baba ba, musamman waÆ™ar sa ta Tsumagiya, Isra’i, Imamul Mursalina da sauran É—imbin waÆ™oÆ™in sa. 

 

Mu na fatan Allah ya sanya shi cikin Dhiyafar Sayyiduna RasululLahi (SallalLahu AlaiHi Wa AaliHi Wa Sallam) Ya sabunta rahma a gareshi, Ya jiƙan sa, Ya kai rahama kabarin sa. Allah Ya albarkaci zuriyar sa, Ya bai wa dukkan Musulmi haƙurin jure wannan babban rashin da aka yi.


Daga:

Khalifah Zubairu M Sani

Labari


©Fatimiyyaa

Comments