TAMBA YOYIN KOTU WA SHAIDAN FARKO.



 Tambayoyin kotu ga sheda na farko:


1. Alkali: "Shin alkawari zaka dauka cewa zaka fadi gaskiya ko rantsewa zakayi da Alqur'ani?"


Amsar sheda: "Alkawari zan dauka zan fadi gaskiya".


Nan take Alkali ya umarci registrar daya alkawarantar da sheda.


- Registrar ya alkawarantar da sheda kamar yadda doka ta tanada.


2. Kotu ga masu gabatar da kara: "Kotu ta baku damar gabatar da sheda na farko.


3. Lauyan masu kara:

- Shin kasan wanda ake kara?


Amsa:" eh na sansh"


- lawyer: ya sunan sa?


Amsa: Abdujabbar Kabara


- lawyer: "Mai ka san ya nayi, ma'ana aikinsa?


Amsa: "Malami ne mai karantarwa.


- Lawyer:

" A ina yake karantarwa?


Amsa:

" A Jami'u Ashabulkahfi da Jami'ur Rasuul.


Lawyer: "wuraren da ka ambata a wanne gari suke?


Amsa: " A nan Garin Kano


Lawyer: "ya akayi kasan yana karantarwa?

- "Na sani ne saboda ina makotaka da Ashabulkahfi, kuma akwai yan uwana da abokai ba wadanda dalibansa ne.


Lawyer: Tunda kace kai makwabcinsa ne, shin kana halartar karatuttukansa ne?

 Amsa: " eh ina halartar karatuttukansa.


Lawyer: "Shin zaka iya tinawa a ranar 08/10/2019 da misalin karfe hudu na yamma ko makamancin haka, ka fadawa kotu abinda ya faru?


Amsar sheda: "Wannan ranar juma'a ce bayan nayi sallar La'asar a inda nake sana'a ta a Sani Mainagge tsallaken tsallaken go dan kankara. Na tsallako domin sauraron karatu Kamar yadda na saba.


Bayan an karbi gaisuwa da addu'o i ga jarirai da aka haifa. Sannan Malam ya fara bayani akan mas'alar auren Annabi (SAW) da Nana Safiyya. Sheda ya maimaita kalmomi da aka sa a wurin mukabala (kamar su Kwace, Fyade, Auren Dole).


Da yake kokarin yin Karin haske ga kotu, sheda na farko yace:

”Wanda make kara yace: "Nana Safiyya tazo a kaso na wani Sahabi, sai Annabi (SAW) yasa aka kwato masa ita. Ya musanya masa da kuyangu guda 16. Yace kaga wannan kwace ne  kenan.


Ita kuma yace mata: Daga Yau kin zama mata ta, kuma sadakin ki shine yancin ki. Ya fadi lambar hadisin a Musulim (1365) da kuma (1428) yace sukai ta maimaitawa. Ya kuma ce wannan fyade ne daraja ta daya. Kuma hadisin daya fada babu wannan kalma ta kwace da fyade a cikin hadisin.

Wannan yasa na fahinci shine ya kaga musu.


ZAMU CIGABA....


AKAFSAN REPORTERS

         14/19/2021

Comments