ASHIRYE DALIBAN SHEIKH ABDULJABBAR SUKE SUBARSHI!!

 MEYASA BAMU BAR SHEIKH ABDULJABBAR KABARA BA ?


Dayawan mutane sun yi mamakin meyasa Almajiran Sheikh Abduljabbar kabara basu barshiba. faruwan wannan waki'ar?


bugu da kari ma sai imani da tafiyar da wasu suka kara yi du da Cewa ga zargin da akewa malamin nasu ga kuma halin da yake ciki 


To abin da mutane wasu suka gaza fahimta shine Alhamdulillah ba alfahari ba maganar gaskia duk Wanda ka gani gaban mallam Abduljabbar daidai gwargwado ba jahili bane kuma yana da hankali ba mahaukaci bane , kuma shiya zo da kan shi ba jawo shi mallam Abduljabbar yayi ba ba kuma a gidan TV sunnah ko redio yaji muryar shi ba 


Tsawan shekara sama da biyu ana Karatun Jauful Farah Wanda sheikh Abduljabbar kabara ya ke gabatarwa , sannan shekara biyu baya yayi Rayuwa bayan mutuwa Wanda a cikin wadan nan Karatukan ne aka datsi wasu gurare aka jona aka sakarwa duniya cewa yau ga sheikh Abduljabbar kabara ya zagi Annabi saw  dan cimma wata manufa tasu ta ganin bayan Sheikh Abduljabbar din 


Sunyi tsammanin taron mabiyan sa zasu watse ne su bar shi shi kadai to sai Allah yasa mabiyan nasa sun San me dukkanin abin dake faruwa Kana kuma Karatun sheikh Abduljabbar din ba Wanda basuji ba ba Wanda basu dashi , ga duk dalibin sheikh Abduljabbar kabara yasan awanna karatu ne  aka Ciro wadan nan maganganun aka jona kuma tuni ya saurara ya wuce gurin yayin da aka kawo mai second 30 ko 40 aka ce ga malamin Ku fa yace da Annabi kaza shi yana ji yasan inda aka Ciro maganar kuma nayi imanin saiya kare maganar bama sheikh Abduljabbar ba dan haka hankalin sa bazai tashi ba domin yasan karya ce


Sun yi kokarin kunya ta shi gurin Mukabala ta yadda zasuyi masa daurin talala ta inda bazai iya taba kare kan shi ba a idon duniya , suka yaudare shi da yadda tsarin mukabalar zai kasance sai bayan ya isa gun suka sanar dashi an canza tsarin Wanda a lokacin suka so yace bazai zaman ba domin su kama shi suce yaji tsoro , to kuma daya amince zai zauna din sai suka zabi yan jaridun da suke so su zasu shiga gun sannan sai abin da suke so shi zasu yada a haka akai zaman jaridu sukai ta wallafa karya kuma suka dauko kasurgumin dan Izala wai shine alkalin Mukabalan


Alokacin babu dalibin sheikh Abduljabbar din da hankalin sa bai tashi ba magana daya sheikh Abduljabbar yayi bayan Mukabala ta kwantar mana da zukata 


Duk Wanda kasan yana bin sheikh Abduljabbar kabara tun daga Mukadimma zuwa Jauful Farah wallahi bazai bar shi ba dan wannan  waki'ar ta faru domin yasan shiri ne irin na magautan sa da dadden shiri 


Dan haka mu diban sheikh Abduljabbar kabara a shirye muke mu bar shi idan aka tabbatar mana da hadisan daya Kore gaskia ne kuma ga fiqhun su a musulinci  


Rida'ul kabeer 

Sakaratul mautt 

Shiga Gidan Ummu HARAM

Hadisin Fitsari a tsaye 

Hadisin iyayen Ma'aki saw 

Hadisin Annabi Nada shaidan 


Wadan hadisan Da Sheikh Abduljabbar kabara ya Kore su a hakkin ma'aiki saw wallahi in su kadai ya Kore zuwan sa duniya kawo yau Wallahi  har duniya ta tashi bazan daina kaunar Sheikh Abduljabbar 


Ina Kaunar sheikh Abduljabbar kabara Fiye da wadda nake masa a 2020.

Comments