KIRARINDA SHEIKH DR ABDULJABBAR YAKEYIWA ANNABI SAW.


 KIRARINDA SHEIKH ABDULJABBAR 

YAKEYIWA ANNABI SAW.KAMARDA KOWA YASANSU.


"Dukkanin yabonmu da godiyarmu su taho gunsa mafi yabo

ÆŠan Abdu mai babban rabo


Baban MuÉ—allabi 

Jikan MuÉ—allabi

Ja gaba Manzonmu mai cetonmu


ÆŠa tilo maras tamka, uban É—akin dukkanin Annabawa


Shugaba ga Mala'iku

Na Khadijah

Jikan Nuhu

Goyon Amina 'yar Wahabu

Sarkin muminai


ÆŠa mai biyayya

ÆŠa abun bi

ÆŠan halas mai kyan hali, mai kyan halitta

ÆŠa fari, mai kyan kulawa, mai kala, wane dala

Wane dalandalami na gogaggar azurfa mai kala


Goshinsa das

Fuskarsa tas

Hancinsa É—as

Ga kyan hakora jeraras


Gemunsa ya cika, yayi lub-lub, yayi daidai, yayi kyau, ba ya kama da na bunsurai.


Ƙyallinsa na haskakawa idan yayi murmushi

Ga kyan wushirya

Ga kalan lebensa ja zur

Ga idonsa gada-gada tamkar farin nono

Farinsu kal, bakinsu ƙirin, girarsa a lanƙwashe


Gashin Muhammadu [S] yafi izga

Ƙyalli da sheƙi

Walwalin fuskarsa yafi matsoƙaci


Harshensa ja

Farchensa ja da fari kamar dinariya


Naman jikinsa a É—aure

Shi ko yana dire


Bai zanƙale a tsawo ba

Bai diƙis-diƙis a dirinsa ba

Maganarsa tamkar yayyafin da yake zuba

Lafazin sa yafi zuma daÉ—i idan ya fit da shi


Kyawun sa shine kyau

Gare shi ka fit da dukkan kyau ga shi É—an Abdu

Baban FaÉ—ima, na Khadijah


Babu kamar ya kai ï·º"


~Dr Sheikh Abduljabbar Kabara (H).

©Fatimiyya Alawuyya tv

Comments