MACIJIYA ZATA FITO TA CINYE WANDA YA KARYATA HADISAN ABUHURAIRA


 MACIJI ZAI FITO YA SARE KA, IDAN HAR KA SAKE KA ƘARYATA HADISIN SAHABI ABUHURAIRA (RTA) 


Saifullahi Murtala Jibia


Masu ƙaryata Hadisin Anas suna cin bulus to , idan kuka sake kuka ƙaryata Hadisin Abuhurairai, akwai bi-baya, saboda haka, a yi hattara  !!!


 Kamar yadda ya zo a ( سير أعلام النبلاء )

Na Al-Hãfizuzzahabi (R) yã tabbatar cewa, wata macijiya mai girma ta biyo wani saurayi, akan yã  ƙaryata hadisin sayyidna Abuhuraira. To  yãya aka ƙarke ??


قال الحافظ أبو سعد السمعاني : سمعت أباالمعمر المبارك بن أحمد.سمعت أبا القاسم يوسف بن علي الزنجاني الفقيه سمعت

الفقيه أبا إسحاق الفيروزابادي ، سمعت القاضي أباالطيب يقول : كنا في مجلس النظر بجامع المنصور ، فجاء شاب خراساني ، فسأل عن مسألة المنصورة، فطال بالدليل، حتي استدل بحديث أبي هريرة الوارد فيها ،


Na ji Al-Ƙãdy, Abaɗɗayyibi, yana cewa : Mun kasance a majlisi na munãzarã tsakanin malamai, A Jãmi'ul Mansúr. Sai wani matãshī mutumin Irãn yã zo,. Sai ya yi tambaya  a kan Aimamma (dabbar da aka ba wa wani nau'i na abinci ,don tabayyanar da ƙibar da ba ta al'ada ba ).Aka ce masa , ai idan mutum ya sayi dabba aimamma ,yana da ikon ya je ya tayar da cinakin  to mene ne hujja ? Sai aka kafa masa hujja da Hadisin Abīhuraira.


فقال- وكان حنفيا :   (( أبوهريرة غير مقبول الحديث )). فمااستتم الكلامه حتي سقط عليه حية عظيمة من سقف الجامع. فوثب الناس من أجلها،

 


Saurayin ya kasance Bahanafe ne, sai  ya ce : (( Ai bã á kar6ar Hadisin Abuhuraira )) bai rufe bakinsa ba , sai ga wata shirgegiyar macijiya,tã fãɗó daga kan rufin Masallãci, sai mutane suka watse (ridididididi ) !!


وهرب الشاب منها وهي تتبعه، فقيل له : تب تب. فقال : تبت، فغابت الحية ، فلم يرلها أثر. إسنادها أئمة.


Shi ma saurayi, sai ya girka dagudu. Ai kuwa sai macijiyar ta biyo shi. Ana cikin haka, sai Jama'a suka ce wa saurayin : KA CE MATA , KÃ TŪBA , KÃ TŪBA. SAI YA CE (( NÃ TÚBA )). Sai macijiyar ta bace. Ba a kuma ganinta ba daga wannan ranar  !!!!


Isnãdin wannan magana duka A'IMMATU ne suka ruwaito.IN JI ALHÃFIZ (R) (( 2/618-619 )).


 Anan ne Dr.Abduljabbar (H) ya ce : Bai dãce ba, mu mayar da Addinin mu ire-iren waɗannan tatsunniyoyi ba,To idanmacijiya zata bayyana har da biyo wani  saurayi, saboda  kawai ya ce, ba a karbar Hadisan Abuhuraira,TO SAYYID NA UMAR FA, DA YA CE ZAI ROTSA KAN ABUHURAIRA, IDAN YA KUMA ZANTAR DA HADISAN ANNABI (SAW)


A wannan littafin dai (Siyaru A'lãmun Nubala) na Zahabin (( 2/600-601 )) ?????


سعيد بن عبد العزيز : عن إسماعيل بن عبيد الله عن السائب بن يزيد ، سمع عمر يقول لأبي هريرة :لتتركن الحديث عن رسول الله (ص) أو لألحقنك بأرض دوس.  


Daga Sa'ibu Bn Yazid,Ya ce, ya ji sayyid na Umar Yana ce wa Abuhuraira :" KO DAI KA DAINA ZANTAR DA HADISAN NAN DA KAKE CEWA DAGA ANNABI (SWA), KO IN MAIDA KA GARINKU " !!


يحيي بن أيوب : عن ابن عجلان : أن أبا هريرة كان يقول : إني لأحدث أحاديث، لو كلمت بها في زمن عمر ،لشج رأسي.


Yahya Ibn Ayyub, daga Ɗan Ijlãn ya ce : Lallai Abuhuraira ya kasance yana cewa, NI BÃ NA ZANTAR DA HADISAI, DÃ NÃ SAKI NÃ ZANTAR ZÃMANIN UMAR , DA YA ROTSA MANI KAI NA". (( 2/601 )).


TO IDAN DAI WANCAN MACIJIN NA GASKIYA NE , ME YA SA BAI FITO BA, YA BIYO UMAR (RTA) WAN DA  SHI  BAYAN  RASHIN  YARDA  DA HADISAN MA, HAR DA SHARADIN DUKA ????


Yau , ko dã babu Kafurai mã su ƙoƙarin rosa mana Addini, to ya dãce mu cire irin waɗannan ƙarairayi daga litattafan mu na addini.


AS'HABULKAHFI JIBIA SOCIAL MEDIA TEAM JIBIA , 07/09/2021, .  

Fatimiyya Alawuyya TV

Comments